5.4.18
AyAU Alhamis
LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa
JARIDAR HAUSA TA FARKO MAI FITOWA KULLUM A NIJERIYA
www.leadershipayau.com Leadership A Yau
5 Ga Maris, 2018 (18 Ga Rajab, 1439)
LeadershipAyau
No: 119
N150
Baquwar Cuta Ta Halaka Mutum 10 A Jigawa Daga Munkaila Abdullah, Dutse
Rahotanni sun bayyana cewa, kimanin mutane goma ne aka tabbatar da sun rasa rayukansu yadda wasu kuma da dama ke kwance a asibiti don karvar magani sakamakon varkewar wata baquwar cuta a qauyukan Baro, Ari, Gamji da Maule dake qaramar hukumar Babura a jihar Jigawa.
Shugaban qaramar hukumar ta Babura Alhaji Muhammed Ibrahim ya tabbatar da afkuwar al’amarin ya yin zantawarsa da ma nema labarai ta wayar salula. Shugaban ya bayyana cewa, zuwa yanzu dai basu sami tabbacin musabbabin cutar ba sakamakon sai ma’aikatar lafiya sun gwada sannan su bada bayanai a matsayinsu na masana fannin lafiya. Rahotanni sun bayyana cewa, baquwar cutar ta
bayyana ne kwatsam a qauyen Baru yadda wasu mutanen suka fara da zazzavi da kuma amai yadda kafin wani qanqanen lokaci sai mutum ya ce ga garin kunan. Haka kuma bayanai sun nuna cewa, a wannan qauye na baru an rasa rayukan mutane matasa maza su huxu. Haka kuma, bayanai sun nuna cewa, sakamakon vullar cutar a garuruwan Ganji da Maule yadda
anan kuma aka rasa rayukan mutane biyar. Shi ma wani mazaunin qauyen Hardo Umar ya bayyanawa majiyarmu cewa,a halin da ake ciki a yanzu akwai mutane uku da ya sani suna can Asibiti suna karvar magani. LEADERSHIP A Yau , ta yi iya bakin qoqarinta domin ganawa da kwamishinan lafiya na jihar Dakta Abba Zakar don jin matakan da suka xauka amma har zuwa loakacin haxa wannan rahoto al’amarin ya ci tura.
Rashawa Ta Fi Cutar –Magu Kansa Illa 4
• Shugaban Hukumar Yaqi Da Cin Hanci Da Rashawa, Ibrahim Magu (a tsakiya); Daraktan Sashe na LEADERSHIP A Yau, Mubarak Umar (na biyu a dama); Editan Jaridar LEADERSHIP A Yau, Sulaiman Bala Idris (na farko a hagu) tare da Editan Jaridar LEADERSHIP A Yau LAHADI, Malam Nasir Gwangwazo (na farko a dama) jiya a yayin wata ziyarar musamman da tawagar LEADERSHIP A Yau ta kai wa Shugaban a hedikwatar EFCC dake Abuja
’Yan Fashi Sun Kai Hari Sanata Mustapha Bukar Ya Rasu Wani Coci A Abuja > Shafi na 5
> Shafi na 14