19.4.18
AyAU Alhamis
LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa
JARIDAR HAUSA MAI FITOWA KULLUM TA FARKO A NIJERIYA
www.leadershipayau.com Leadership A Yau
19 Ga Afrilu, 2018 (2 Ga Sha’aban, 1439)
LeadershipAyau
No: 127
N150
Jonathan Ne Silar Wahalhalun Da Ake Sha A Nijeriya –Tinubu Daga Umar A Hunkuyi
Shugaban Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya sake xora zarginsa kan gwamnatin farar hula da ta gabata, kan matsalar tattalin arzikin qasarnan da ake fama da shi a halin yanzun. Tinubu, ya bayyana hakan ne cikin jawabin sa, a matsayin sa na babban baqo a taron shekara-shekara na 35 na tunawa da Malam Aminu Kano,
wanda aka yi ranar Talata a Kano. Tinubu, wanda Gwamnan Jihar Oyo, Sanata Abiola Ajimobi, ya wakilce shi, ya bayyana cewa, gwamnatin tsohon Shugaban qasarnan, Goodluck Jonathan, ita ce babbar mai laifi wajen wawashe albarkatun qasarnan. Masu jawabi a wajen taron su ne, mawallafin kafar yaxa labaran nan ta, Premium Times, Mista Dapo Olorunyomi; da kuma wani babban
jigo a Jam’iyyar APC, Dakta Usman Bugaje, duk sun yi nazarin mulkin Dimokuraxiyya ne a qasarnan, da kuma matsayin aqidar Jam’iyyun siyasa. Tinubu, ya danganta rashin samuwar manyan ayyuka a qasarnan kan bilyoyin kuxaxen da gwamnatocin baya suka sace.
>Ci gaba a shafi na 2
•Tinubu
Zargin Badaqalar Biliyan 18:
EFCC Za Ta Fara Farautar Kwankwaso Da Wamakko 4
•Shugaban Qasa, Muhammadu Buhari a wurin taron dandamalin kasuwanci na qasashe rainon Ingila wanda ya gudana jiya a Xakin Taro na Guild Hall dake Landan
Yadda Aka Kashe ’Yar Shekara 2019: Ya Kamata A Haxa Qarfi Uku Da Fyaxe A Kano Don Korar Buhari –Falae > Shafi na 2
> Shafi na 2