3.4.18
AyAU Talata
LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa
JARIDAR HAUSA MAI FITOWA KULLUM TA FARKO A NIJERIYA
www.leadershipayau.com Leadership A Yau
3 Ga Afrilu, 2018 (16 Ga Rajab, 1439)
LeadershipAyau
No: 117
N150
Sunayen Mutanen Da Ake Zargi Da Satar Kuxin Gwamnati Daga Umar A Hunkuyi
Gwamnatin tarayya ta qara sakin wasu sabbin sunayen na mutanan da ake zargi da tsiyata lalitar qasarnan, a zamanin mulkin tsohon Shugaba Godluck Jonathan. Ministan yaxa labarai, Lai Mohammed, ne ya bayyana
sunayen, ya kuma zargi Jam’iyyar adawa ta PDP, a bisa martanin da ta yi wa sunayen farko da gwamnatin ta saki. Sabbin sunayen da Ministan ya shelantawa duniya guda 23 ne. Gwamnatin ta tarayya ta ce, sunayen mahandaman da ta saki tun da farko, an tabbatar da su ne,
gami da bayyana yawan kuxaxen da suka handama, lokaci da kuma wajen da suka yi satan. Da yake bayyana sabbin sunayen mahandaman, a wani bayanin da ya fitar a Legas ranar Lahadi, Lai Mohammed, ya ce, masu qorafin sunayen farkon da aka saki sun yi kaxan, ba su fahimci dubarar da
ake yi ba ne wajen sakin sunayen a matsayin xanxano. “Ai ko a lokacin da na saki sunayen na farko, na ce wannan somin tavi ne, amma ai gwamnatin tarayya tana da dogon jadawalin sunayen mahandaman a hannunta.
>Ci gaba a shafi na 5
Zamfara:
Har Yanzu Ana Tsinto Gawarwaki A Daji 4
Boko Haram Ta Kashe Mutum 28 A Borno Daga Muhammad Maitela, Maiduguri
Aqalla mutum 28 ne suka rasa rayukan su, inda wasu qarin wasu mutum 55 suka samu raunuka daban-daban, a wani sabon farmakin da mayaqan qungiyar Boko Haram suka kai a qauyen Bale, wanda ya ke kusa da Maiduguri, babban jihar Borno. An kai harin ne da kimanin qarfe 8:00 na daren ranar lahadi. Bayanai sun bayyana cewa an xauki awanni ana jin qarar harbe-harben bindiga masu sarrafa kan su da qarajin tashin abubuwa masu fashewa-babu qaqqauta wa, bayan babban birnin jihar. Wata qwaqqwarar majiyar tsaro ta tsegunta wa kamfanin dillacin labarai na Nijeriya (NAN) kan cewa wasu ayarin mayaqan Boko Haram ne suka dumfari qauyukan BaleShuwa da Bale-Kura, waxanda da ke kusa da Maiduguri, a yunqurin su na kutsa kai cikin birnin, Dan misalin qarfe 8:00 na daren. • Al’ummar garin Anka yayin da suke haqa qaburburan da za su bizne gawarwakin da aka tsinto daga dazuka.
>Ci gaba a shafi na 2
Dole Mu Qarfafi Matasa Su ‘Noma Ne Ya Ceto Nijeriya Daga Karayar Tattalin Arziki’ Karvi Shugabanci –IBB > Shafi na 6
> Shafi na 14