30.03.18
AyAU JUMA'A LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa
www.leadershipayau.com Leadership A Yau
JARIDAR HAUSA
LeadershipAyau
30 Ga Maris 2018 (12 Ga Rajab, 1439)
TA FARKO MAI FITOWA KULLUM A NIJERIYA
Bugu na: 029
N150
PDP Tuban Muzuru Ta Yi, In Ji Bola Tinubu Daga Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
Babban Jigon Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya shawarci ‘yan Nijeriya da kada su karvi tuba da afuwar da Jam’iyyar PDP ta yi masu kan kura-kuran da ta tafka a yayin da take kan karagar mulki. Tinubu ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis Lagas a wajen taron qarawa juna
sani kan bukin murnar cikarsa shekaru 66 a duniya. Wakilinmu ya labarto cewar Shugaban Jam’iyyar PDP na Qasa, Mista Uche Secondus a ranar Litinin xin da ta gabata a Abuja ya nemi gafarar ‘yan Nijeriya kan kura-kuran da jam’iyyar ta tafka a yayin da take saman mulki. A kan wannan Tinubu ya bayyana tuban
babbar jam’iyyar adawar a matsayin wata sabuwar yaudarar da suka vullo da ita da nufin neman sake samun tasiri a siyasance. Babban jigon na APC ya qara da cewar PDP ta durqusar da Nijeriya ta hanyar cin hanci da rashawa da ya yi katutu a mulkin ta yana cewar kada a bari su sake dawowa saman mulki domin tubansu na mazuru ne. >Ci gaba a shafi na 4
Ana Zargin Dakarun Soji Da Luguiguita Mutane A Katsina 5
Shugaban Qasa Muhammadu Buhari, mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbanjo tare da Bola Ahmed Tinubu (a tsakiya), yayin gudanar taron qoli na jagoran APC, Bola Tinubu jiya a otel xin Eko da ke Birnin Ikko.
Dino, Tsuntsun Da Ya Jawo Ruwa Shi Ruwa Kan Doka – Gwamnan>Kogi Shafi na 4 Yadda Aka Yi Jana’izar Sojojin Ahlul Faidati Sun Buxe Mauludin Da Aka Kashe A Kaduna> Shafi na 4 Shehu Ibrahim Na Bana A Kano > Shafi na 2